Sauya fasalin noma na daga cikin manyan manufofin Atiku ga Najeriya- Baraka Sani

Hajiya Baraka Sani
Hajiya Baraka Sani

Daraktar Kungiyoyin Tallafawa, ta kwamitin yakin neman zaben Shugaban kasa na Jam’iyyar PDP Hajiya Baraka Sani ta ce kawo sauyi a harkar noma na daga cikin manyan manufofin cigaba guda biyar na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar.

Baraka Sani ta bayyana hakan ne a Kano karo na farko a gangamin taron kananan manoma, a jihar, mai taken “Tsare tsaren inganta fannin noma:”

Ta ce manufar Atiku na inganta ci gaban sassan tattalin arziki, noma, ma’adanai, masana’antu, kananan masana’antu, matsakaita da kananan masana’antu tare da hadin gwiwar bangarori daban-daban don samun tattali me inganci.

Ta kara da cewa idan takarar jam’iyyar PDP ya lashe zabe, zai bunkasa samar da abinci duk shekara ta hanyar fadada wuraren noman rani, domin rage tasirin sauyin yanayi da kuma tsawaita lokacin shukar zuwa duk shekara.

A nasa bangaren, babban bako mai jawabi, Farfesa Muhammad Sanusi Gaya a cikin kasidar da ya gabatar mai taken “inganta irin shuka, maganin ci gaban noma mai dorewa” ya ce amfani da tsofaffin iri da manoma ke yi a Najeriya ne ya sa harkar noma ba ta bunkasa.

“Mun ga a wasu kasashe manoma suna samun tan 10 na amfanin gona iri daya da muke noma a nan, yayin da muke samun kilo 200 kawai, wani manomi a wani wurin kuma yana samun lita 20 na madara daga saniya.

“Iraruwan da muke amfani da su sun tsufa kuma sun tsufa, karfin kwayoyin halitta yana raguwa.”

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here