Gwamnatin Saudiyya ta yi watsi da jita-jita game da dakatar da aikin Umrah saboda karuwar COVID-19.
Wata majiya a ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta shaida wa Haramain Sharifain cewa ba ta da niyyar dakatar da Umrah.
Don haka ta yi kira ga maziyarta da mahajjata da su bi matakan kariya da hukumomin da suka dace suka dauka.
Kwanan nan ne Fadar Shugaban Masallatan Harami guda biyu ta sake dawo da matakin bayar da tazara da a Masallatan Harami guda biyu bayan an samu bullar cutar COVID-19.
“Muna kira ga kowane mahajjaci da bako da su ringa bayar da tazara tare da sanya abin rufe fuska a kowane lokaci domin hakan zai tabbatar da tsaron ku da lafiyar sauran,” Limamin Masallacin Harami Sheikh Yasir Al Dossary ya sanar kafin fara sallar la’asar Alhamis.
Saudiyya ta ba da sanarwar mutuwar mutane biyu daga COVID-19 da sabbin cututtukan 5,499 a ranar Alhamis.
Daga cikin sabbin masu cutar da aka samu, 1,565 a Riyadh, 877 a Jeddah, 474 a Makkah, 239 a Madina, 198 a Dammam, 137 a Taif, 110 a Qatif, 103 a Al-Khobar, 102 a Hofuf, 100 a Khulais. Wasu garuruwa da yawa sun sami adadin sabbin kararraki kasa da ɗari kowanne.
Adadin wadanda suka warke daga cutar ya karu zuwa 555,035 bayan wasu karin marasa lafiya 2,978 sun murmure daga cutar. Kimanin mutane 8,901 ne suka kamu da cutar a kasar ya zuwa yanzu.
Sama da allurai miliyan 53.3 na allurar rigakafin coronavirus an gudanar da su a cikin Masarautar zuwa yau.
Babbar fadar shugaba mai kula da al’amuran masallacin Harami da masallacin Annabi sun kara shiryawa masu ziyara maraba da zuwa lokaci mai zuwa ta hanyar sabunta kayan aikin wuta da injina da na lantarki.













































