Mambobin majalisar masarautar Olubadan da suka koma matsayin Oba sun amince su yi watsi da rawaninsu su koma kan manyan sarakuna.
An yanke wannan shawarar ne a wani taro da majalisar ta gudanar a fadar Oja’ba na Olubadan na Ibadanland ranar Alhamis.
Taron ya samu halartar wakilai wakilan majalisar su 6, Wanda suka hada da Owolabi Olakulehin (Balogun na Ibadanland), Tajudeen Ajibola (Otun Balogun), Lateef Adebimpe (Osi-Balogun), Kola Adegbola (Ashipa Balogun), Eddy Oyewole (Ashipa Olubadan) da Hamidu. Ajibade (Ekarun Olubadan).
Idan dai za a iya tunawa, Otun Olubadan, Sanata Lekan Balogun, a baya ya ce Obas din da abin ya shafa a shirye suke su koma mukaminsu na asali bisa umarnin gwamnan jihar, Seyi Makinde na cewa su koma.
Otun Balogun, Tajudeen Ajibola, wanda ya bayyanawa manema labarai bayan taron, ya ce sun goyi bayan gwamnan kan matakin da ya dauka na komawa ga asalin al’adar Ibadan.
A cewarsa, ‘Mun amince da gwamnan. Dukkan hanyoyin da suka kai ga nadin magajin marigayi Olubadan sun yi daidai da ainihin manufar layin sarauta kamar yadda sanarwar sarauta ta Olubadan ta tanada.













































