Hukumar kula da Yanayi ta ƙasa (NiMet) ta yi hasashen cewa za a samu Hazo a sararin samaniya da gajimare daga ranar Litinin zuwa Laraba a faɗin ƙasar nan.
A rahoton yanayi da ta fitar a ranar Lahadi a Abuja, NiMet ta ce za a samu ɗan ƙura kaɗan a yankin Arewa a ranar Litinin a duk tsawon lokacin hasashen.
Hukumar ta ce wasu jihohi kamar Borno da Yobe za su fuskanci ƙura mai matsakaici, inda hangen nesa zai kasance tsakanin kilomita 2 zuwa 5.
Ta ce a yankin Arewa ta Tsakiya ma za a samu ɗan ƙura kaɗan a duk lokacin hasashen.
A yankin Kudu kuwa, ana sa ran yanayi mai gajimare tare da ɗan hasken rana lokaci-lokaci, tare da ƙaramin yiwuwar tsawa da safe a wasu sassan Cross River da Akwa Ibom.
Ta ƙara da cewa daga baya a rana za a samu tsawa mai ɗauke da ruwan sama kaɗan a sassan Ondo, Ogun, Lagos, Edo, Bayelsa, Cross River, Rivers, Delta da Akwa Ibom.
A ranar Talata NiMet ta yi hasashen ƙura mai matsakaici a yankin Arewa, inda hangen nesa zai kasance tsakanin kilomita 2 zuwa 5.
A Arewa ta Tsakiya kuwa za a samu ɗan ƙura kaɗan.
A Kudu kuma za a samu gajimare tare da hasken rana lokaci-lokaci, tare da yiwuwar tsawa da safe a Akwa Ibom da Cross River.
Daga baya za a samu tsawa mai ruwan sama kaɗan a sassan Lagos, Oyo, Ondo, Ogun, Edo, Bayelsa, Cross River, Rivers, Delta da Akwa Ibom.
Ranar Laraba, hukumar ta ce za a samu ƙura mai yawa a yankunan Arewa da Arewa ta Tsakiya a duk tsawon lokacin hasashen.
A Kudu kuma za a samu gajimare tare da hasken rana lokaci-lokaci, da yiwuwar tsawa da safe a Cross River da Akwa Ibom.
Daga baya za a samu tsawa mai tafe da ruwan sama kaɗan a sassan Bayelsa, Lagos, Ondo, Ogun, Edo, Cross River, Rivers, Delta da Akwa Ibom.
NiMet ta shawarci jama’a da su ɗauki matakan kariya saboda ƙurar da ke yawo a sararin samaniya a yankunan Arewa, Arewa ta Tsakiya da kuma jihohin cikin ƙasar a Kudu.
Ta kuma gargadi masu fama da cutar asma da sauran matsalolin numfashi da su yi taka-tsantsan.
Hukumar ta ce direbobi su yi tuƙi a hankali yayin ruwan sama, sannan ta shawarci kamfanonin jiragen sama da su riƙa samun rahoton yanayi na filayen jiragen sama daga NiMet domin tsara ayyukansu yadda ya kamata.













































