Jami’an hukumar yaƙi da hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kama wasu mutum huɗu da ɗaruruwan katunan cirar kuɗi domin sayen ƙuri’a a jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya.
A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce an loda wa kowanne kati naira 10,000, tare da saka masa lambobin sirri, waɗanda ake zargin na sayen ƙuri’a ne.












































