Hukumar kiyaye haddura ta tarayya, (FRSC) reshen jihar Ondo, ta ce akalla mutane 13 ne suka kone kurmus a hanyar Ikare-Akoko/ Owo ranar Asabar a jihar.
Samuel Ibitoye, kwamandan hukumar FRSC reshen jihar ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai ranar Asabar a Akure.
“Hukumar FRSC ta yi nadamar sanar da jama’a wani hadarin mota da ya afku a yau Dec.28, a Abule Panu gaban gadar Ose, kan babbar hanyar Owo-Ikare, jihar Ondo.












































