Kungiyar matuka baburan adaidaita sahu ta jihar Kano ta yi alkawarin hada kan mambobinta domin baiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da dan takarar gwamnan jihar Kano, Dr Nasiru Gawuna, kuri’u Dubu 500 a 2023.
Shugaban kungiyar Alhaji Mansir Tanimu ya yi wannan alkawari lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga Manajan Darakta na hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Jihar Kano (KAROTA) wanda ke rike da mukamin Daraktan kungiyar yakin Neman zaben Tinubu na Arewa maso Yamma, Bappa Babba Dan agundi a ofishinsa.
Ya ce matakin ya zama dole domin mayar da biki kan sauraron korafe-korafen mambobinta da kuma alkawarin da gwamnatin jihar ta yi na duba hanyoyin da za a tallafa musu don inganta harkokinsu.
A cewarsa, “Babban dalilin da ya sa muka zo nan a yau shi ne mu gode wa gwamnatin jihar bisa sauraron korafin da muka yi kan dakatarwar da ta yi a kwanakin baya da kuma alkawarin da ta yi na tallafa wa mambobinmu da motocin haya da motocin bas don bunkasa sana’arsu ba tare da an rage musu adadinsu ba.
Ya ce kungiyar za ta ba Tinubu da Gawuna kuri’u 500,000 kowannensu saboda masu yin rajistar babur suna da karfin da za su iya ba da kuri’u.
Don haka ya yabawa mambobinsu da rashin shiga yajin aiki ko zanga-zanga a lokacin da gwamnati ta hana su gudanar da ayyukan wasu manyan tituna a cikin birnin, wanda a cewarsa, shi ne dalilin da ya sa gwamnati ta saurari kokensu tare da sauya umarnin.
A nasa jawabin, Dan Agundi ya yabawa jami’an da suka kawo musu ziyara tare da ba su tabbacin gwamnatin jihar na goyon bayansu da nufin inganta harkokinsu