Babbar kotun tarayya dake zamanta a Abuja, a yau Talata ta bawa DSS dama su cigaba da rike Tukur Mamu, mai sasan ce tsakanin ‘yan ta’adda da iyalan wadan da akai garkuwa dasu a jirgin kasan Abuja-Kadun, zuwa nan da kwanaki 60.
Mai shara’a Nkeonye Maha ya bada umarnin ne biyo bayan lauyan hukumar tsaro ta farinkaya ya nemi da a kara musu lokaci don cigaba da binkice akan Tukur.
Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN ya ruwaito cewa ‘yan sandan Masar sun kama Tukur Mamu tare da iyalansa a ranar 6 ga watan Satumba, ya yin da yake kan hanyar sa ta zuwa Saudiyya domin yin Umara, daga karshe suka dawo dasu gida Najeriya.
A ranar Lahadin ta gaba ta jami’an na hukumar ta DSS suka jawa ‘yan Najeiya kunne kan tufar albarkacin bakin su akan kama Tukur Mamu.













































