Gwamnatin tarayya ta ce hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta gano jami’o’i kusan 70 da suka sabawa doka da kuma kwalejojin ilimi kusan 125 da ke aiki a kasar nan.
Ministan Ilimi, Adamu Adamu ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin taron karawa juna sani na majalisar Zartarwar Kasar nan karo na 47 a Abuja.
Adamu ya ce haramtattun jami’o’in da ya bayyana a matsayin “Degree Mills” na kawo babban kalubale ga kokarin da ma’aikatar ke yi na ganin an samu damar samun ilimin jami’a ba tare da wata matsala ba.
A bayanan karshe da hukumar ta NUC ta wallafa dangane da makarantun boko da cibiyoyin karatun da aka yi su ba bisa ka’ida ba, a shekarar 2021, hukumar ta bayyana sunayen jami’o’i 58 da ta rufesu da kuma jerin sunayen wasu cibiyoyi 8 da har yanzu ake ci gaba da bincike kan zargin kasancewarsu na bogi.













































