Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da sallamar nan take ga ɗaya daga cikin mataimakansa, Adamu Abdullahi Danko, mai ba shi shawara na musamman mataki na biyu kan harkokin gida, tare da wasu mutum uku, bayan kammala bincike kan dukan da aka yi wa Ho. Abdulrahman Abubakar Sheriff, kansilan mazabar Shamaki a ƙaramar hukumar Gombe a jihar.
Wannan mataki ya fito ne a cikin wata sanarwa da Darakta Janar kan harkokin yaɗa labarai na gwamnan, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar.
Sanarwar ta bayyana cewa Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ne ya isar da shawarar bayan kafa wani kwamiti na musamman domin binciken lamarin.
Jam’iyyar APC a jihar Gombe ta yi Allah wadai da harin da aka kai wa kansilan mai ci a kan kujerarsa, wanda wani mataimakin gwamnan ya aikata, lamarin da aka ɗauka a bidiyo kuma ya bazu sosai a kafafen sadarwa na zamani.
Bidiyon ya nuna Adamu Abdullahi Danko, wanda ke aiki a ofishin Shugaban Ma’aikata na gwamnan, yana dukan kansilan cikin halin rashin ƙarfi, abin da ya janyo ce-ce-ku-ce da suka haɗa da kiran a ɗauki matakin ladabtarwa a kansa.
Ƙungiyoyin fararen hula da suka haɗa da Amnesty International da Cibiyar Ƙungiyoyin Fararen Hula ta Jihar Gombe sun yi Allah wadai da zargin dukan, suna neman a tabbatar da adalci tare da ɗaukar mataki mai tsauri kan wanda ya aikata laifin, suna bayyana lamarin a matsayin nuna rashin bin doka da ƙaruwa a danniya daga jami’an gwamnati.
Rahoton kwamitin bincike, wanda rahotannin hukumomin tsaro suka ƙara tabbatarwa, ne ya sa gwamnan ya ɗauki wannan mataki, inda sauran da abin ya shafa su ne Garba Mohammed Mai Rago, Rabiu Sulaiman Abubakar da Ali Ibrahim Baban Kaya, dukkaninsu mataimaka na musamman mataki na biyu.
Gwamnan ya umurce su da miƙa dukkan kayan gwamnati da ke hannunsu nan take, yana jaddada ƙudirin gwamnatinsa na bin doka, gaskiya da zaman lafiya a jihar.













































