Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya taya Dr Muhammad Jameel Yusha’u, dan asalin Kano murna, wanda ya karbi mukamin babban jami’in tantance ingancin labarai, edita a fitacciyar mujallar siyasa ta Africa, dake Havard.
Acikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Abba Anwar ya fitar a ranar Juma’a, ta ce kasancewarsa dan Arewa na farko da ya samu mukamin a Harvard, Gwamna Ganduje ya ce, “Muna alfahari da samun gwarzon malami matashi irinka da suka yi fice a fagen duniya.”
‘’ Ya ji dadi matuka kuma ya bayyana Yusha’u a matsayin ƙwararre wanda ya sauya harkar yada labarai da harkar sadarwa izuwa halin inganci datake ciki yanzu. Mun kuma samu labarin cewa ya taka rawa kwarai a lokacin da yake rike da mukamin babban jami’in kula da tsare-tsare na bankin ci gaban Musulunci, in ji sanarwar.
Jaridar Solacebase ta rawaito cewa Yusha’u, babban malami ne a fannin yada labarai da siyasa a jami’ar Northumbria da ke birnin Newcastle na kasar Birtaniya kuma malami a fannin aikin jarida na duniya na jami’ar Sheffield. Bayan ya bar Najeriya a matsayin malami a tsangayar sadarwa ta Jami’ar Bayero dake Kano.
A cewar sanarwar, ya yi rubuce-rubuce da dama da ya daga darajar sa a mujallun nazarin kafofin watsa labarai da sadarwa na duniya, kamar su Global Media Studies, Journal of Arab and Muslim Media Research, da dai sauransu.
“Don haka a madadin gwamnatin Kano, ina taya Dakta Muhammad Jameel Yusha’u murnar samun wannan matsayi mai girma na Babban Editan Jaridar Siyasa ta Afrika da ya fito daga arewacin Najeriya.













































