Farfesa Ibrahim Gambari, tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa ga marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa dimokuraɗiyyar Najeriya za ta iya dorewa ne kawai idan aka ci gaba da bin tsarin jam’iyyu masu yawa da ake da shi a halin yanzu.
Gambari ya bayyana hakan ne a taron shekara-shekara na tattaunawa kan Abiola Ajimobi da kuma bikin cikar marigayi tsohon gwamnan shekaru 76 bayan rasuwarsa, wanda aka gudanar a cibiyar Albarkatun Sanata Abiola Ajimobi da ke Jami’ar Ibadan, inda ya jaddada muhimmancin samun jam’iyya mai mulki tare da adawa mai ƙarfi da tasiri.
Ya yi gargaɗi cewa tsarin jam’iyya ɗaya zai iya janyo illa mai tsanani ga tsarin dimokuraɗiyyar ƙasar, yana mai cewa rashin adawa mai ƙarfi na rage sahihanci da ingancin shugabanci a ƙasa.
A cikin takardar da ya gabatar mai taken hanyar tabbatar da sahihancin zaɓe, tsohon ministan harkokin waje ya jaddada buƙatar sake fasalin tsarin zaɓe ta hanyar kawar da rashin sha’awar siyasa, wanda ya danganta da son kai, rashin haɗin kai, tilasta shugabanci da kuma rashin dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyun siyasa.
Sai dai Gambari ya yabawa marigayi Abiola Ajimobi kan sadaukarwarsa ba tare da son rai ba, tare da bayyana gadon da ya bari na ladabi, jarumtaka da hangen ci gaba, wanda ya buɗe hanya ga ci gaban jihar Oyo da Najeriya baki ɗaya.
Shirin tattaunawar, wanda shi ne karo na takwas a jerin tarurrukan, kuma karo na biyar tun bayan rasuwar Ajimobi, an shirya shi ne domin girmama tasirinsa, haɗa iyalansa da kuma wayar da kan jama’a kan salon shugabanci da tafiyar da mulki.
A jawabinsa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda shugaban hukumar tara haraji ta ƙasa Zach Adedeji ya wakilta, ya bayyana Ajimobi a matsayin jajirtaccen dan siyasa wanda ya yi mulki da ƙarfin hali tare da hidima mai cike da sadaukarwa, yana mai jaddada wasu tsare-tsaren ci gaba da suka kawo sauyi mai kyau ga siyasar jihar Oyo da ci gaban jihar.
Tun da farko, gwamnan jihar Oyo Seyi Makinde, wanda mataimakinsa Barrista Bayo Lawal ya wakilta, ya bayyana Ajimobi a matsayin shugaba mai hangen nesa da jajircewa wajen hidimar jama’a.
Ya kuma ce, ƙoƙarin sauyi da ya yi a fannoni daban-daban ya haifar da gado mai ɗorewa da gwamnatinsa ke ci gaba da gina kai.












































