Farfesar Da Aka Kora Kan Batanci Ga Annabi Za Ta Maka Jami’arta A Kotu

Jamiar Hamline da ke birnin Minnesota a Amurka
Jamiar Hamline da ke birnin Minnesota a Amurka

Erika Lopez Prater, Farfesar nan da aka kora daga Jami’ar Hamline da ke Amurka saboda nuna zanen Annabi Muhammad (S.A.W) yayin koyarwa ta ce za ta maka makarantar a kotu.

Jami’ar dai, wacce mai zaman kanta ce a birnin St Paul na Jihar Minnesota a Amurka, ta yanke shawarar korar malamar ne bayan korafin da ta samu daga daya daga cikin dalibanta kan nuna hoton.

Erika Lopez dai ta nuna hoton ne a daya daga cikin azuzuwan da take koyar da Tarihi, lamarin da bai yi wa dalibai Musulmai na ajin dadi ba.

Ga Musulmai da dama dai, nuna hoto ko wani zane da ke nuna Annabi haramun ne kuma suna daukarsa a matsayin batanci ga addininsu.

Sai dai a kwafin karar wacce malamar ta ce nan ba da jimawa ba za ta shigar, ta jaddada cewa ba ta aikata ba daidai ba, saboda sai da ta yi gargadi kafin ta nuna hotunan, ta yadda ko da wani ba ya son ganin su zai iya fita.

Karar ta kuma yi zargin cewa korar ta jawo wa Erika matsala a rayuwar aikinta a matsayin malama, kuma hakan na iya jawo mata tsangwama da bakin jini a nan gaba.

Lauyoyin Farfesar, sun fada a cikin sanarwar cewa, “Daga cikin abubuwa da dama, hukumomin Jami’ar Hamline sun gwammace su shafa wa Erika Lopez kashin kaji, ta hanyar bayyana ta a matsayin wacce ya tsani Musulunci.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here