Tsohon gwanan jihar kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce bai je rantsar da Abba Kabir Yusuf bane sabo da jin tsoron kada rigima ta shi a tsaknanin magoya bayan su.
Gandujen ya shaidawa a hakane a wata hira da ya yi da BBC Hausa, inda ya ce bashi da wata matsala da sabowar gwamanatain ta kano.
Ya kara da cewa “Mika mulki ya kasu gida biyu, na farko shine mika mulki wanda ya kunshi bada takardu da duk wani bayanai na gudanarwar gwamnati, wanda ya hada da aiyukan ada aka agama da wanda ma ba’a gama ba, da kuma shawar-ware da ake bawa gwamantin da za’a rantsar.”
“Kashi na biyu kuma shine rantsuwa. Indan gwamanatin da zata tafi idon ba jama’iyyar su daya da wacce za’a rantsar ba, ya zama dole kada a halarci taron rantsuwar domin tsoron samun hatsaniya a tsakanin magoya bayan mu.”
Ya yin da aka tambaye shi akan ko ya zo rantsar da Tinubu ne domin neman mukami, sai Gandujen ya ce ” Ni ban zo nan saboda neman mukami ba, amma idon aka bani zan karba”
“Ina kyuatatawa gwamnatin Tinubu zato. kuma muna yi masa addu’a samun nasara a gwamnatin sa, kuma zamu cigaba da bashi taimako domin an zabe shine sabo da ya shuka abin alkairi a baya.”













































