Dalilin da ya sa na rushe majalisar zartarwa- Bago

Bago 750x430

Gwamna Umaru Bago na jihar Neja ya ce, ya rusa majalisar zartarwarsa ne a tsakiyar wa’adi na duba ayyukan gwamnatinsa.

Bago ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin a Minna.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa gwamnan, a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Ibrahim Bologi, ya fitar, ya sanar da rusa majalisar ministocinsa a yayin zaman majalisar zartarwa ta jihar.

Sai dai Bago ya rike manyan jami’ai da suka hada da sakataren gwamnatin jihar, shugaban ma’aikata, mataimakin shugaban ma’aikata, da sauran manyan jami’ai a ofishinsa.

Gwamnan ya ce za a iya sake nada wasu daga cikin mambobin majalisar yayin da wasu kuma za a iya sanya su a ma’aikatu daban-daban.

Ya ce gwamnati tana da faɗi, kuma ana iya tura mutane zuwa ma’aikatu daban-daban.

Bago ya nuna jin dadinsa ga mambobin majalisar da ke barin gado bisa gudunmawar da suka bayarwa wajen ci gaban jihar.(NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here