Gwamna Umaru Bago na jihar Neja ya ce, ya rusa majalisar zartarwarsa ne a tsakiyar wa’adi na duba ayyukan gwamnatinsa.
Bago ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin a Minna.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa gwamnan, a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Ibrahim Bologi, ya fitar, ya sanar da rusa majalisar ministocinsa a yayin zaman majalisar zartarwa ta jihar.
Sai dai Bago ya rike manyan jami’ai da suka hada da sakataren gwamnatin jihar, shugaban ma’aikata, mataimakin shugaban ma’aikata, da sauran manyan jami’ai a ofishinsa.
Gwamnan ya ce za a iya sake nada wasu daga cikin mambobin majalisar yayin da wasu kuma za a iya sanya su a ma’aikatu daban-daban.
Ya ce gwamnati tana da faɗi, kuma ana iya tura mutane zuwa ma’aikatu daban-daban.
Bago ya nuna jin dadinsa ga mambobin majalisar da ke barin gado bisa gudunmawar da suka bayarwa wajen ci gaban jihar.(NAN)













































