Gwamnatin tarayya da Hukumar dakile cin hanci da karbar rashawa ta ICPC sun fara wani yunƙuri don bankado lamuran karkatar da kudade da suka shafi shirin N-Power.
Jaridar Solacebase ta rawaito cewa shirin N-Power wani shiri ne da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kafa a ranar 8 ga watan Yuni, 2016, domin magance matsalolin rashin aikin yi da matasa ke fuskanta da kuma taimakawa wajen bunkasa zamantakewa.
Wata sanarwa da babban sakatare a ma’aikatar jin kai, Dr Nasir Sani-Gwarzo ya fitar, ta ce an samu sabani iri iri a tsarin biyan masu cin gajiyar N-Power.
Sanarwar ta ce wasu ma’aikatan Hukumar Biyan Kuɗi ne suka aiwatar don haka akwai bukatar a gayyaci hukumar da ke yaki.
Sanarwar ta ce, Sani-Gwarzo ya kuma yi kira ga al’umma da su rika kai rahoton duk wasu kura-kurai da suka faru dangane da shirin ta kowace hanya kamar haka: npowersupport@nsip.gov.ng ko npowerinfo@nsip.gov.ng ko kuma a kira 07030859183.













































