Hukumar jami’ar gwamnatin tarayya dake Dutsinma a jihar Katsina, ta tabbatar da kubutar sauran Daliban jami’ar Mata dake hannun masu garkuwa.
Shugaban jami’ar Farfesa Armaya’u Hamisu Bichi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai ranar juma’a a Katsina.
Yace dalibai matan da suka shaki iskar yancin wasu ne daga cikin Dalibai biyar da aka yi garkuwa da su a baya.
Karanta wanannan: Hedikwatar tsaro ta tabbatar da hallaka Manyan Kwamandojin ‘Yan Ta’adda
Tun a ranar 3 ga watan Oktoban da ya gabata ne aka yi garkuwa da daliban a gidan da suke haya dake kusa makarantar Mariyamu Ajiri memorial, dake Dutsinma.
Hamisu yace yanzu haka za’a duba lafiyar su kafin damka su a hannun iyalan su.
Kamfanin dillancin labarai NAN ya tuna cewa tun a ranar 3 ga watan Oktoban shekarar 2023, ‘yan sanda suka tabbatar da yin garkuwa da ‘yan matan.
Kazalika a ranar 20 ga watan Nuwambar da ya gabata ‘yan sandan suka tabbatar da kubutar daya daga cikin daliban dakd hannun masu garkuwar.












































