DA DUMI-DUMI: Mahaifiyar dan majalisar dokokin Kano da aka sace ta sake samun ‘yanci bayan an biya kudin fansa

91715842 54AF 4085 8DCF 14D97D27E31A
91715842 54AF 4085 8DCF 14D97D27E31A

Mahaifiyar dan majalisar dokokin Kano da aka sace, Hajiya Zainab, ta samu ‘yanci bayan an biya ta kudin fansa.

An sace Hajiya Zainab, mahaifiyar Isiyaku Ali Danja, shugaban marasa rinjaye, majalisar dokokin jihar Kano a gidanta da ke karamar hukumar Gezawa a Kano, a ranar 12 ga Janairu, 2021.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga Solacebase a ranar Talata, dan majalisar ya ce mahaifiyarsa ta samu ‘yanci bayan an biya N40m.

Ali Danja wanda shi ne kakakin majalisar ya ce suna kan hanyarsu ta dauko ta ne daga wata karamar hukuma da ke jihar Jigawa inda masu garkuwa da mutane suka ajiye ta.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here