Da ɗumi-ɗumi: Saudiyya ta ayyana Juma’a a matsayin ranar Eid-el-Fitr

moon sighting

Kotun koli ta Saudi Arabia ta sanar da cewa za a gudanar da bikin Eid-el-Fitr a ranar Juma’a, 20 ga Maris, 2026, bayan da ba a samu sahihin rahoton ganin jinjirin watan Shawwal a fadin ƙasar ba.

A cewar wata sanarwa ta hukuma, kwamitocin duban wata sun gudanar da aiki a wurare 12 a duk faɗin ƙasar, amma babu wani sahihin shaida da aka samu na ganin jinjirin daga kowanne yanki.

Bayan faduwar rana, manyan masana ilimin taurari da aka tanada domin duban wata sun hallara a wuraren lura da sararin samaniya a sassa daban-daban na ƙasar, ciki har da Tumair, Sudair, Shaqra, Umm al-Qura, Al-Wajh, Halat Ammar, Qassim, Dammam, Madinah da Hail domin ganin watan.

Duk da wannan ƙoƙari da aka yi a dukkan wuraren, ba a tabbatar da ganin jinjirin da ke nuna fara watan Shawwal ba.

Kotun kolin ta duba duk rahotannin da aka gabatar kafin ta yanke hukuncin cewa watan Ramadan zai cika kwanaki 30 a wannan shekara.

Saboda ba a ga jinjirin Watan a ranar 29 ga Ramadan ba, watan zai kammala adadinsa na kwanaki 30.

Musulmai a Saudiyya, tare da sauran ƙasashen da ke bin sanarwar ƙasar, za su gudanar da Eid-el-Fitr a ranar Juma’a bayan kammala kwanaki 30 na azumi da ibada.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here