Sama da mutane 25 ne suka mutu sakamakon ballewar cutar diphtheria a jihar Kano ranar Juma’ar data wuce.
Jaridar Solacebase ta tattaro rahotan cewa cutar dake kashe kanan yara wcce aka gano ta a shekarar 2022, ta sake ballewa bana a Kano, inda yanzu haka ake bawa wadan da suka kamu da ita kulawar gaggawa a asbitin kwararru na Murtala Muhammed da kuma asibitin koyarwa na Aminu Kano Teaching Hospital, AKTH, a jihar Kano.
Kwararun likitoci sun bayyana cewa wannan cutar dake harbar hanci da makogaro za’a iya samun kariya daga kamuwa da ita ta hanyar amfani da manganin garkuwa wato (vaccine.)













































