Yan bindiga sun hallaka muntane 60 a kasuwar Goronyo

Dead bodies in Sokoto
Dead bodies in Sokoto

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin yaran gawurtaccen dan ta’addan nan Turji, ne sun kashe fiye da mutane 63 a harin da suka kai babbar kasuwar Goronyo da ke jihar Sokoto.

Yan ta’addan da yawansu ya kai dari, sun mamaye kasuwar da misalin karfe 4:50 na yammacin jiya Lahadi dai-dai lokacin da mutanen kauyen ke harkokinsu na saye da sayarwa a cikin kasuwar inda suka bude musu wuta.

Rahotonni sun ce ‘yan bindigar sun kwashe kusan sa’o’i biyu sun cin karensu ba babbaka ba trae da kai daukin jami’an tsaro ba, wadanda ba a iya sanar da su harin ba sakamakon rufe hanyoyin sadarwa na yankin.

A cewar jaridar DailyStar, majiya daga Karamar Hukumar, ta ce an kirga gawarwaki arba’in tun a daren jiya Lahadi.

Haka kuma, wasu daga cikin mazauna garin na Goronyo sun tabbatar da cewa tuni aka adana gawarwaki 62 a babban Asibitin Goronyo zuwa safiyar yau Litinin, baya ga wasu gawarwakin da danginsu suka tafi da su domin yi musu jana’iza.

Majiyoyin sun kuma ce akwai wasu da dama da har yanzu ba a gano su ba yayin da suke kokarin tsere wa ta hanyar shiga cikin ‘yan fashin dajin yayin da suke harbin.

Sun kara da cewa wasu na karbar magani a asibiti, wadanda da yawa daga cikinsu suna cikin mawuyacin hali na jin jiki.

Solacebase ta ruwaito cewa kasuwar Goronyo sananniyar kasuwa ce wajen cinikayyar albasa da shanu.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here