Majalisun kasa: CISLAC, TI sun nuna damuwa game da barazanar da ke karuwa ga ma’aikatan majalisa, masu mataimawa ‘yan majalisar

EEAA41AA 2DA4 428B 9553 53860F79ABFF
EEAA41AA 2DA4 428B 9553 53860F79ABFF

Kungiyar Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC) da kungiyar Transparency International a Najeriya sun nuna matukar damuwa da takaicin yadda mahukuntan majalisar dokokin kasar ke ci gaba da tursasa wa jami’an majalisar da kuma masu  mataimaka masu tare da tabarbarewar walwala da  ci gaban ma’aikatan.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Darakta na CISLAC kuma shugaban kungiyar Transparency International a Najeriya Auwal Ibrahim Musa (Rafsanjani) ya fitar kuma ya aika zuwa ga Solacebase a ranar Lahadi.

“Ba mu da masaniya game da wata takarda mai taken “RANTSUWA GA SIRRI” wanda Sakataren, Ma’aikata da magatakarda na Majalisar Dokoki ta kasa suka yi  gargadin ma’aikatan / mataimakan majalisa da su bi umarnin rantsuwar sirri ta hanyar kiyaye cikakken sirrin abubuwan da ya shafi jin dadin su; da kuma kauracewa yin amfani da kafafen sada zumunta wajen bayar da bayanai,” in ji sanarwar.

“Mu ba tare da wani yankuri na murkushewa tare da tursasawa ma’aikata da mataimaka don bibiyar muhimman hakkokinsu, wanda hakan babban cin zarafi ne ga sashe na 34, 37 da 39 na kundin tsarin mulkin 1999, wanda ke tabbatar da ‘yancin mutunta bil’adama.

Sanarwar ta ce, ”Muna nuna damuwa ga dimokuradiyyar kasa idan aka mayar da irin wannan furuci na rashin gaskiya cikin al’ada, aiki da ayyukan Majalisar Dokoki ta kasa, a matsayin babbar bangaren majalisa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here