Irin nasarorin da na samu a Legas zan iya maimaita su a fadin Najeriya – Tinubu

Bola Tinubu new new
Bola Tinubu new new

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC a zaben 2023 Asiwaju Bola Tinubu ya ce nasarorin da ya samu a matsayinsa na gwamnan jihar Legas za su iya maimaituwa a Najeriya idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Tinubu ya bayyana haka ne a farkon Jawaban da ya gabatar na yakin neman zaben sa wanda aka kaddamar a Abuja.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya rawaito cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya kaddamar da takardar mai shafi 80 a hukumance tare da jiga-jigan jam’iyyar da manyan jami’an gwamnati a dakin taro na Banquet Hall dake Abuja.

Tinubu ya ce a shirye ya ke ya maimaita irin bajintar da ya yi na tsawon shekaru takwas a jihar Legas a fannin daban daban dan sauya fasalin kasar.

A cikin Jawabin nasa mai shafuka 20, dan takarar shugaban kasa ya lissafa tsarin kiwon lafiya, ilimi da samar da gidaje a matsayin muhimman wuraren da zai fi mayar da hankali.

”Abin da ni da tawagara muka cimma a Legas, tabbas tare duk za mu iya sake maimaita makamancin sa a Najeriya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here