Mazauna Kano sun yi mamaki a daren ranar Alhamis yayin da birnin ya samu ruwan sama na farko a shekarar 2026, lamarin da ba kasafai ake gani ba a watan Maris, musamman a Kano da mafi yawan sassan arewacin Najeriya.
Jaridar Solacebase ta rawaito cewa ruwan saman, wanda ya fara kusan karfe 9 na dare, ya dauki kimanin mintuna 30 kafin ya tsaya.
Sai dai yawan ruwan ya bambanta a sassa daban-daban na birnin, inda mafi yawan wurare suka samu saukar dan ruwan sama kadan maimakon ruwan sama mai yawa.
Mutane da dama sun bayyana lamarin a matsayin abin mamaki, suna mai cewa ba kasafai ake samun ruwan sama a watan Maris a Kano ba.
A al’ada, damina a Kano da yawancin yankunan arewa mai nisa na Najeriya kan fara ne tsakanin karshen watan Mayu zuwa farkon watan Yuni bayan watanni na zafi da fari mai tsanani.
Ko da yake wasu sassan arewacin Najeriya, musamman yankin Middle Belt da wuraren da ke kusa da tsakiyar Najeriya kamar Abuja, na iya samun ruwan sama da wuri a wasu lokuta, amma samun ruwan sama a watan Maris abu ne da ba kasafai yake faruwa ba a Kano saboda yanayinta na Sahel.
Wannan lamari ya zo ne makonni kadan bayan hukumar kula da hasashen yanayi ta Najeriya NiMet ta gabatar da hasashen yanayi na kakar shekara ta 2026, inda ta yi gargadin yiwuwar sauye-sauyen tsarin ruwan sama, tsawon lokacin fari, tsananin hutun damina na watan Agusta a wasu sassan kasar, da kuma yawan zafi a fadin Najeriya.
Hasashen wanda aka gabatar a ranar 10 ga Fabrairu a Abuja ya bukaci masu ruwa da tsaki da suka hada da manoma, hukumomi masu kula da bala’o’i da masu tsara manufofi su shirya domin yiwuwar hadurran da suka shafi sauyin yanayi a cikin shekarar.
Jaridar Solacebase ta rawaito cewa irin wadannan hasashe na nuna muhimmancin sa ido sosai kan sauyin yanayi yayin da al’ummomi a arewacin Najeriya ke ci gaba da fuskantar tasirin sauyin yanayi.
Masana yanayi sun bayyana cewa saukar ruwan sama da wuri ba lallai ba ne ya nuna cewa an samu cikakken sauyi a tsarin yanayi, amma yana iya kasancewa sakamakon sauye-sauyen yanayi na lokaci-lokaci.
Sun bayyana cewa wani lokaci irin wadannan ruwan sama na wuri kan faru ta dabi’a, amma karuwar faruwar yanayi a shekarun baya-bayan nan na kara tayar da hankali kan tasirin sauyin yanayi.
Masana sun kuma bayyana cewa sauyin yanayi na ci gaba da shafar lokacin da ruwan sama ke sauka da kuma karfinsa a yankin Sahel, ciki har da arewacin Najeriya.
Sun ce karuwar zafin duniya na lalata tsoffin tsarin yanayi, wanda wani lokaci kan haifar da saukar ruwan sama da wuri, tsawon lokacin fari ko kuma ruwan sama mai karfi cikin kankanin lokaci.
A cewarsu, sauye-sauyen tsarin ruwan sama na iya haifar da matsaloli ga noma da kuma albarkatun ruwa a arewacin Najeriya, inda yawancin ayyukan noma ke dogara da ruwan sama na kakar damina.
Ruwan sama na wuri na iya sa manoma su fara shuka da wuri fiye da yadda aka saba, amma amfanin gona na iya lalacewa idan ruwan saman ya tsaya na dogon lokaci.
Masana sun kuma yi gargadin cewa yanayin da ba a iya hasashe ba na iya shafar samuwar ruwa, kiwon dabbobi da kuma tsaron abinci a yankin.
Saboda haka masana sun jaddada bukatar samar da dabarun daidaitawa da sauyin yanayi masu karfi daga al’ummomi da kuma hukumomin gwamnati.
Sun ba da shawarar kara inganta sa ido kan yanayi, yada bayanan gargadi da wuri ga manoma da kuma kara zuba jari a hanyoyin noma da za su iya jure sauyin yanayi.













































