Tsohon ministan wasanni, Bolaji Abdullahi, ya bayyana cewa an cire shi daga muƙaminsa a zamanin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ne bayan ya ƙi fitowa fili ya kai hari ga tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki a lokacin wani kamfen na siyasa a jihar Kwara.
Abdullahi, wanda tun da farko ya riƙe muƙamin ministan raya matasa kafin a sauya masa aiki zuwa ma’aikatar wasanni, an sauke shi daga muƙaminsa a watan Maris na shekarar 2014.
Ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a wani shirin siyasa na gidan talabijin, inda ya ce an ɗauki matakin ne sakamakon matsin lambar siyasa da ta taso bayan Saraki ya fice daga jam’iyyar PDP ya koma APC.
Ya kuma ce, ziyarar da shugaban ƙasa Jonathan ya kai jihar Kwara domin kamfen na PDP ta zo dai-dai da lokacin da Saraki ya sauya sheƙa, lamarin da ya haifar da tsammanin cewa shi ne zai jagoranci yaƙi da tsohon ubangidansa a siyasa.
Abdullahi ya ce an ɗauke shi a matsayin babban jami’in siyasa mafi girma daga jihar Kwara a wancan lokaci, inda ake sa ran zai karɓi tsarin PDP a jihar, ya tallafa da kuɗi, tare da jagorantar kamfen ɗin shugaban ƙasa, amma ya ƙi yin hakan saboda ka’ida da ra’ayi na kashin kansa.
Ya ƙara da cewa yanayin siyasar a lokacin ziyarar ya kasance mai tsauri, inda ‘yan jam’iyya ke kai hare-hare ga Saraki, kuma ana matsa masa lamba ya shiga cikin wannan lamari, amma ya zaɓi tsayawa kan abin da ya yi imani da shi.
Tsohon ministan ya bayyana cewa wannan matsaya tasa ta sa ya shiga mawuyacin hali tsakanin biyayya ga Saraki da kuma rawar da yake takawa a cikin majalisar zartarwa ta gwamnatin tarayya, yana mai cewa irin wannan yanayi na tilasta ɗaukar ɓangare a rikicin siyasa na zuwa da tsada.
Duk da an cire shi daga muƙami, Abdullahi ya ce bai yi nadamar yin aiki a gwamnatin Jonathan ba, yana mai cewa tun da farko ya riga ya fahimci abin da zai iya faruwa bayan ya ƙi ɗaukar ɓangare, tare da jaddada cewa ya shafe shekaru yana aiki tare da Saraki a matsayin mataimaki na musamman kan sadarwa, mai ba da shawara kan manufofi, da kuma kwamishinan ilimi a lokacin da Saraki yake gwamnan jihar Kwara.
A halin yanzu, Abdullahi wanda ke riƙe da muƙamin sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar ADC, ya ce shawarar da ya ɗauka a wancan lokaci ta samo asali ne daga ƙwaƙƙwaran ra’ayi na kai, ba don sauƙin siyasa ba, duk da cewa hakan ya janyo masa rasa matsayinsa a majalisar zartarwa ta gwamnatin tarayya.













































