Rundunar Ƴan Sanda ta Jihar Kanio ta cafke wani matashi ɗan shekara 18, Saminu Bala, bisa zargin kisan abokinsa a Kofar Mazugal a birnin Kano.
Daily Trust ta rawaito cewa Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da kisan cewa cacar-baki ce ta ɓarke tsakanin Bala da marigayi Ibrahim Khalil sai shi Bala ɗin ya daki Khalil, lamarin da ya janyo mutuwar sa.













































