Jam’iyyar ADC ta bukaci shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, Farfesa Joash Amupitan, da ya yi murabus nan take tare da dukkan kwamishinonin hukumar na ƙasa.
Jam’iyyar ta kuma bukaci dukkan kwamishinonin INEC na ƙasa su yi murabus, tana mai cewa shugabancin hukumar ya mayar da kansa kayan aiki a hannun jam’iyyar APC mai mulki.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Sanata David Mark, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai na duniya da aka gudanar a Abuja a ranar Alhamis, inda ya nuna rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da harkokin zabe a ƙasar.
Jaridar Solacebase ta rawaito cewa jam’iyyar ta zargi shugabancin INEC da karkata bangare daya, tana mai cewa hukumar ta zama kayan aiki a hannun jam’iyyar APC mai mulki.
Ya ƙara da cewa wannan hali na iya kawo barazana ga dimokuraɗiyyar Najeriya, idan har ba a dauki matakin gyara ba cikin gaggawa.
Sanata David Mark ya kuma yi kira ga ƙasashen duniya da su sanya ido tare da taimakawa wajen kare tsarin dimokuraɗiyya a ƙasar.
Haka kuma ya bukaci ‘yan Najeriya da kada su amince da duk wani yunƙuri na mayar da ƙasar zuwa tsarin jam’iyya ɗaya sakamakon matakan da ake zargin gwamnatin APC na ɗauka.
Ana sa ran ƙarin bayani kan wannan lamari yayin da ake ci gaba da bibiyar martanin INEC da sauran masu ruwa da tsaki.













































