Kasar Birtaniyya tace tana shirye shirye na rage tsauraran sharuddan da ta gindaya na bulaguron shiga kasar ta hanyar janye takunkuman da ta dora kan wasu kasashe cikin sahun kasashe masu hadarin kamuwa da sabuwar Nau’in cutar Omicron.
Jaridar Daily Mail ta birtaniyya ta rawaito cewa, Sakataren sifiri da zirga zirga na birtaniyya, Grant Shapps na kokarin daidaita al’amura da abokan hulda ta hanyar maye tsarin dakatarwar da yin gwaji kafin shiga kasar.
Rahotanni sun nuna cewa an samu tirka tirka nan_da_can sakamakon sanya wasu kasashe cikin kasashe masu hadarin barazanar kamuwa da sabuwar nau’in cutar, Wanda da dama kasashe ne dasuka fito daga nahiyar Afrika.
Idan za a iya tunawa amakon damukai bankwana ne, Gwamntin Najeriya ta bayyana shirin kakaba takunkumin yin bulaguro na shiga kasashen birtaniyya, Canada da Saudi Arabia farawa daga talata ta makon damuke ciki.
Firaministan birtaniyya, Boris Johnson aranar laraba ta makon jiya, yayi alkawarin sake nazari kan matakan da birtaniyan ta dauka, laakari da yadda al’umma da dama kê kalubalantar matakin dacewa akwai alamun rashin adalci kan daukan matakan.
Ayanzu haka dai, ana sa ran amakon damuke cikine, kasar birtaniyar zata amince da sabbin matakan, na rage tasirin takunkumin hana shiga kasar biyo bayan bazuwar sabuwar nau’in Cutar Omicron.












































