Tsohon ministan yaɗa labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ya bayyana yadda wani abokin aikinsa a majalisar ministocin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari ya yi masa suka ba tare da adalci ba a lokacin taron mako-mako na majalisar zartarwa ta ƙasa.
Ya bayyana hakan ne a cikin littafinsa da aka ƙaddamar kwanan nan mai taken Headlines and Soundbites: Media Moments that Defined an Administration, inda ya kawo abubuwan da ya fuskanta a lokacin da yake aiki a gwamnatin Buhari.
Lai Mohammed ya nuna cewa ministan, wanda bai ambaci sunansa ba amma ya ce daga yankin Kudu maso Yamma yake, ya zarge shi da rashin iya aiki a taron majalisar, duk da cewa a wancan lokacin yana wajen ƙasa yana hulɗa da kafafen yaɗa labarai na duniya da cibiyoyin bincike.
Ya bayyana cewa a cewarsa daga baya ya samu labarin Shugaba Buhari ya katse zancen tare da kare shi, yana mai kafa wata gidauniya da aka cewa yana taka rawar gani wajen kare gwamnati da bayyana ayyukanta ga duniya, abin da ya nuna cikakken goyon bayan shugaban gare shi.
Tsohon ministan ya kara da cewa a tsawon lokacin da ya yi a majalisar ministoci, Buhari ba wai kawai yana yaba masa idan ya yi abin kirki ba ne, har ma yana tsayawa tsayin daka wajen kare shi idan aka taso shi, ciki har da wani lamari da aka shigar masa da ƙorafi inda shugaban ya umarci a bincika lamarin kafin daga bisani a wanke shi.
A cikin littafin, Lai Mohammed ya kuma bayyana yadda Buhari ya yi jinkirin amincewa da mayar da martani ga wata budaddiyar wasiƙa daga tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo, amma daga bisani ya ba shi dama bayan doguwar tattaunawa, inda ya gudanar da martanin cikin kwarewa da ladabi, abin da ya jawo yabo daga mutane da dama.
Ya kuma bayyana wasu misalai da ke nuna yadda marigayi Buhari ke ba shi cikakken goyon baya, ciki har da amincewa da kai ‘yan jarida yankunan da sojoji suka kwato daga Boko Haram da kuma samar da tallafin musamman don aiwatar da manyan shirye-shiryen ma’aikatarsa duk da ƙarancin kasafi.
NAN













































