Wike ya yi bikin cika shekaru 58 da haihuwa, ya ce ba ya nadamar goyon bayan Tinubu

Wike 58th birthday celebration 750x430

Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya bayyana cewa ba ya da wata nadama kan goyon bayan da ya bai wa Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu tun daga shekarar 2022.

Ya bayyana hakan ne a wani biki na musamman da aka shirya domin murnar cika shekaru 58 da haihuwarsa a gidansa da ke Abuja.

Ministan ya jaddada cewa matsayinsa ya kasance ɗaya tun kafin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023, a lokacin zaɓen, har ma bayan kammalawarsa.

Ya nuna cewa bai taɓa sauya ra’ayi ba dangane da abin da ya yi imani da shi a siyasance.

Ya ƙara da cewa dukkanin shawarwarin siyasarsa suna tafiya ne bisa ka’idojin ɗabi’a da gaskiya, yana mai cewa tun daga farko bai ɓoye goyon bayansa ga Tinubu ba.

Ya kuma tuna cewa a lokacin shirye-shiryen zaɓen 2023, shi kaɗai ne daga manyan jagororin jam’iyyar adawa da ya fito fili ya goyi bayan Tinubu.

Wike ya bayyana cewa wannan matsaya ta samo asali ne daga adalci, daidaito da gaskiya, tare da imanin cewa ya dace mulki ya koma yankin Kudu.

Ya nuna cewa an ga irin jagorancinsa a jihar Rivers a lokacin zaɓe, inda APC ta lashe zaɓen shugaban ƙasa, yayin da PDP ta samu nasarori a majalisar dokoki ta ƙasa, gwamnan jiha, majalisar dokokin jiha da ƙananan hukumomi a ƙarƙashin jagorancinsa.

Ya gode wa abokansa na siyasa da abokan aikinsa bisa tsayin dakan da suka nuna masa tsawon lokaci, yana mai yaba rawar da suka taka wajen gina tafiyar shugabancinsa.

Ya ce yana jin cikar buri wajen aiki tare da mutanensa, kuma ya yi alkawarin ci gaba da haɗin kai da su domin amfanin al’ummar Rivers da Nijeriya baki ɗaya.

Ministan ya bayyana cewa suka da zagi ba sa damunsa, domin irin waɗannan abubuwa ne ke ƙara masa ƙwazo.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya rawaito cewa manyan jagorori daga bangarorin siyasa daban-daban sun halarci bikin domin taya tsohon gwamnan Rivers murna da yabon tasirinsa a siyasa, inda aka kammala taron da addu’o’i na musamman a gare shi da iyalansa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here