Zaftare albashin ma’aikatan ƙungiyar ƙwallon ƙafar Barau FC ya haifar da cece-kuce

Barau FC

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta shiga rudani sakamakon fushin da ya wanzu a tsakanin ma’aikata da jami’ai kan zaftare albashi da aka yi musu ba tare da bayani ko sanarwa daga shugabancin ƙungiyar ba.

Wasu daga cikin ma’aikatan da abin ya shafa sun bayyana cewa sun yi mamakin ganin an rage albashinsu, inda suka nuna rashin jin daɗi kan yadda shugaban ƙungiyar, Shawwal Barau Jibrin, da babban manaja, Dominic Iorfa, ba su fito sun yi wani cikakken bayani ba game da matakin ba.

Wannan lamari ya ƙara ta’azzara tashin hankali a cikin ƙungiyar, wadda a halin yanzu ke fama da raunin sakamako a filin wasa tare da rarrabuwar kai a harkokin cikin gida.

A martaninsa, shugaban ƙungiyar, Shawwal Barau Jibrin, ya tabbatar da cewa an rage albashin, yana mai bayyana cewa matakin ya shafi ma’aikata da jami’an da ba su taka rawar gani yadda ya kamata ba.

Ya bayyana cewa shugabancin ƙungiyar ya zuba jari mai yawa a cikin Barau FC, amma duk da haka sakamakon wasanni bai gamsar ba, yayin da ƙungiyar ke ci gaba da fafutukar tsira daga sauka daga matakinta.

Shugaban ya ƙara da cewa wanda ya kafa ƙungiyar na da manyan fata da buri, kuma yana da niyyar yin duk mai yiwuwa domin ganin ƙungiyar ta yi nasara, amma ayyukan da ake gani a halin yanzu sun yi ƙasa da abin da ake bukata.

Wasu majiyoyi daga cikin ƙungiyar sun bayyana cewa rikicin cikin gida ya ƙara muni ne jim kaɗan bayan naɗin Dominic Iorfa a matsayin babban manaja, inda wani taro da shugaban ƙungiyar ya yi da sabon manajan da ‘yan wasa ya haddasa ƙarin rashin jituwa, lamarin da ya haifar da rikice-rikice kan iko, yanke shawara, da nauyin aiki, a daidai lokacin da Barau FC ke ƙoƙarin daidaita harkokin cikinta tare da gujewa sauka daga mataki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here