Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umarci manyan jami’an tsaro na ƙasa da su koma Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin su jagoranci yadda za a shawo kan matsalar tsaro bayan hare-haren ta’addanci da suka faru a yankin.
Haka kuma ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ƙungiyoyin masu aikata laifuka da ke aiki a sassa daban-daban na ƙasar nan.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja a ranar Talata, ya bayyana sabbin hare-haren da suka faru a Maiduguri a matsayin abin damuwa matuƙa.
Ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da jajanta wa waɗanda suka jikkata, sannan ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da tallafa musu a wannan lokaci mai wahala.
Ya bayyana cewa hare-haren ta’addanci da ake yi a yanzu ƙoƙarin ƙarshe ne na masu aikata laifuka da ‘yan ta’adda na ƙoƙarin tsoratar da jama’a, yayin da sojoji da sauran jami’an tsaro ke matsa musu lamba a wurare daban-daban.
Ya ƙara da cewa za a ci gaba da ƙara ƙarfi wajen yaƙi da duk wani nau’in masu aikata laifi a ko’ina suke a faɗin ƙasar.
Shugaban ƙasar ya yaba da jarumta da ƙwazon sojoji da sauran jami’an tsaro, musamman yadda suka dakile wasu hare-hare da ‘yan ta’adda suka kai a sansanonin sojoji a jihar.
Ya bayyana hare-haren da suka faru a ranar Litinin a matsayin rashin mafita daga bangaren ‘yan ta’adda, amma ya nuna kwarin gwiwa cewa jami’an tsaro za su shawo kan lamarin.
Ya kuma bayyana cewa ya amince da ƙarin tallafi da kayan aiki ga hukumomin tsaro bayan wani taron tsaro da ya yi da shugabannin hukumomin leƙen asiri da na tsaro.
Ya ce tuni aka fara aiwatar da wannan shiri, tare da umartar shugabannin tsaro su koma Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro, sannan ya umarci hukumomin agaji da su kula da waɗanda suka jikkata yadda ya kamata.
Ya jaddada cewa babu wani wuri a Najeriya da ‘yan ta’adda za su samu mafaka, yana mai cewa za a gano su, a tunkare su, tare da murkushe su gaba ɗaya, kuma ƙasar ba za ta yi kasa a gwiwa ba saboda tsoro.
Wannan umarni ya biyo bayan hare-haren tsaro da suka faru a Maiduguri a daren Litinin, inda fashe-fashe suka auku a kusa da kasuwar Monday Market da kuma wani wurin tsaro a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri.
Rahotanni sun nuna cewa fashe-fashen sun faru da misalin ƙarfe 7 na yamma, sa’o’i bayan wasu da ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kai hare-hare a sansanonin sojoji guda uku a sassa daban-daban na jihar Borno.










































