Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya nuna sha’awarsa na shiga takarar gwamna a 2023.
Dan majalisar ya bayyana hakan ne yayin da yake magana a wata hira da gidan rediyo a Kaduna ranar Asabar.
Shehu Sani ya ce ya shiga takarar ne domin ganin ya ceto jihar daga cikin halin kunci da Gwamna Nasir el-Rufai ya haifar.
Dan majalisar ya bayyana cewa zai yi takara ne karkashin jam’iyyar PDP, inda ya ce ya rage wa jam’iyyar ta hada kan ‘ya’yanta domin kafa gwamnatin da za ta mutunta ra’ayin talakawa a jihar Kaduna.
Ya ci gaba da cewa, “Mun zauna da masoyana da magoya bayana, kuma suna son in tsaya takarar gwamnan jihar Kaduna wanda zan yi don kawar da APC, in Allah Ya yarda; a tsige zababben dan takarar gwamnan jihar sannan ya shiga gidan gwamnati inda za a rantsar da comrade a matsayin gwamnan da zai kawo sauye-sauye, wanda zai share duk wata kazantar da suka kawo jihar da sunan ci gaba.
“Zan kawo tsaro. Wannan shi ne abin da magoya bayana suka so kuma na amince da su.
Don haka zan tsaya takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PDP.
Don haka ina kira ga al’ummar Kaduna da su ba ni goyon baya, su ba ni hadin kai. “Ina kuma rokon addu’arsu; Ina bukatan addu’ar malaman addini, ‘yan kasuwa, nakasassu, mata da matasa.
Kun zabi Malam ne a matsayin gwamna, abin da ya rage a yanzu shi ne a samu abokin zama a matsayin gwamna don ganin bambancin da ke tsakaninmu.
Ya ce idan talaka ya yanke shawarar zabe shi, da kudi ko ba tare da shi ba, zai yi nasara.













































