Sabon labari: Kotun daukaka kara ta tabbatar da hukuncin da ya hana INEC amincewa da taron PDP

PDP PDP 750x430

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin babbar kotun tarayya wanda ya hana Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC amincewa da sakamakon babban taron jam’iyyar Peoples Democratic Party PDP da aka gudanar a Ibadan.

An gudanar da taron ne tsakanin ranar 15 zuwa 16 ga Nuwamba 2025.

A ranar 31 ga Oktoba 2025, mai shari’a James Omotosho na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya hana INEC amincewa da sakamakon taron jam’iyyar na kasa.

A cikin hukuncin da alkalai uku na kotun daukaka kara suka yanke baki daya a ranar Litinin, kotun ta warware batutuwa hudu da ake dubawa a shari’ar ba tare da goyon bayan PDP ba.

Kotun ta ce karar daukaka kara da jam’iyyar PDP ta shigar ba ta da tushe, sannan ta bayyana cewa babbar kotun tarayya ta yi daidai da ta yanke hukuncin ranar 31 ga Oktoba 2025 tare da amincewa da duk bukatun da masu karar suka gabatar.
Kotun ta kuma yi watsi da ikirarin PDP cewa kotun da ta fara sauraron karar ba ta da hurumin yanke hukunci.

A cewar kotun daukaka kara, masu karar suna da hakkin shigar da karar a kotu domin kare hakkokinsu na dimokuradiyya.

Kotun ta kuma yi watsi da ikirarin PDP cewa ba a ba ta damar samun adalci ba yayin sauraron karar a kotun farko.

A wani bangare na hukuncin, kotun daukaka kara ta umarci bangaren PDP da Kabiru Tanimu Turaki ke jagoranta ya biya Naira Miliyan Biyu a matsayin kudin shari’a, inda ta bayyana karar daukaka kararsa a matsayin wadda ba ta da muhimmanci.

Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa NAN ya rawaito cewa taron jam’iyyar ya samar da shugabanni karkashin jagorancin Turaki.

Sai dai wasu mambobin jam’iyyar da ke biyayya ga ministan Babban Birnin Tarayya Nyesom Wike an dakatar da su a lokacin taron, lamarin da ya sa suka kalubalanci matakin a kotu.

A ranar 22 ga Disamba 2025, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC ta yi watsi da bukatar da bangaren Turaki ya gabatar na amincewa da sabuwar kwamitin gudanarwar jam’iyyar na kasa, tana mai cewa akwai hukuncin kotu da kuma wasu matakai na shari’a da har yanzu ba a kammala ba.

Hukumar zaben ta yi nuni da hukuncin babbar kotun tarayya guda biyu da aka yanke a Abuja a watan Oktoba da Nuwamba 2025, wadanda suka hana ta aiwatar da sakamakon taron jam’iyyar da aka gudanar a Ibadan.

Hukumar ta bayyana cewa kasancewar an shigar da kararrakin daukaka kara ba ya nufin dakatar da aiwatar da hukuncin kotunan, tare da jaddada cewa dole ne ta bi doka.

Babbar kotun tarayya da ke zaman ta a Abuja ta soke taron jam’iyyar tare da hana Turaki da sauran jami’an da suka fito daga taron rike mukaman kasa na jam’iyyar.

Sai dai bangaren PDP na Turaki ya ce babu abin tashin hankali, yana mai jaddada cewa tsarin shugabancin jam’iyyar na nan daram.

Bayan wannan hukunci, jam’iyyar ta bayyana cewa ta umarci lauyoyinta su shigar da karar daukaka kara tare da bin duk hanyoyin doka da suke akwai domin kare matsayinta. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here