Rashin tsaro ya tsananta yayin da ’yan bindiga ke ƙara ƙarfi a Arewa

images 1

Ci gaba da hauhawar hare-haren ’yan bindiga a Arewacin Najeriya ya zama ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta, inda hakan ke barazana ga rayuka, hanyoyin samun abinci da kuma zaman lafiyar ƙasa baki ɗaya.

Daga kashe-kashe masu yawa zuwa sace-sacen mutane da kai hare-hare kan ƙauyuka, yawa da tsananin rikice-rikicen sun ƙaru matuƙa a ’yan shekarun nan, lamarin da ya jefa miliyoyin jama’a cikin fargaba da rashin tabbas.

Rahotanni sun nuna cewa abin da ya fara a matsayin aikata laifuka na lokaci-lokaci ya rikide zuwa babbar matsalar tsaro.

Ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da ake kira ’yan bindiga na aiki a jihohi da dama na Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, ciki har da Zamfara, Katsina, Sokoto, Kaduna da wasu sassan Jihar Neja.

Hare-harensu sun haɗa da kai farmaki kan ƙauyuka, satar shanu, garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa, da kai hari kan makarantu da wuraren ibada.

Tsakanin shekarar 2010 zuwa 2023, an danganta mutuwar sama da mutum 13,000 da ayyukan ’yan bindiga, inda hare-haren suka ƙaru sosai bayan 2018.

A baya-bayan nan, hare-haren sun fi zama masu tsanani da muni, inda ake raba al’umma da muhallansu tare da katse harkokin tattalin arziki.

Illolin jin ƙai sun yi tsanani, domin dubban mutane sun tsere daga gidajensu suna neman mafaka a sansanonin ’yan gudun hijira ko garuruwan da ke kusa.

An bar gonaki babu mai noma sakamakon tsoron hare-hare, lamarin da ya taimaka wajen ƙaruwar ƙarancin abinci da yunwa a yankin.

Nazari ya nuna cewa ci gaba da kai hare-hare kan al’umma da gonaki ya zurfafa talauci da koma bayan ci gaba.

A wasu jihohi ma, rashin tsaro ya takaita samun abinci, lamarin da ya ƙara muni ga matsalar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin marasa galihu.

Daga cikin abubuwan da ke haifar da matsalar akwai talauci da rashin aikin yi, musamman a tsakanin matasan karkara da ake sauƙin jawo su cikin ƙungiyoyin aikata laifi.

Raunin tsarin tsaro, iyakoki masu sauƙin tsallakawa, da yaɗuwar ƙananan makamai sun ƙara bai wa waɗannan ƙungiyoyi damar ƙarfafa.

Haka kuma, takaddama kan albarkatu kamar ƙasa da ruwa a yankunan karkara ta ƙara rura wutar rikici.

Masana sun lura cewa duk da cewa ribar kuɗi ce ke motsa yawancin ’yan bindiga, yawan amfani da manyan makamai da dabaru na zamani, ciki har da garkuwa da jama’a masu yawa da kai hare-hare kan cibiyoyin gwamnati, ya sa aka fara rikita bambanci tsakanin aikata laifi da ta’addanci, lamarin da ya ƙara rikitar da magance matsalar.

Duk da matakan soji da tsare-tsaren gwamnati, matsalar na ci gaba da wanzuwa.

A wasu yankuna, ’yan bindiga na ci gaba da rike iko kan wasu wurare, abin da ke sa jami’an tsaro da ma’aikatan agaji wahalar aiki yadda ya kamata.

An kuma sha samun rahotannin cewa har ayyukan ceto da samar da muhimman ayyuka na jama’a na fuskantar tsaiko sakamakon rashin tsaro.

Tasirin hakan ga ci gaban ƙasa yana da zurfi, musamman ma a fannin noma wanda shi ne ginshiƙin tattalin arzikin Arewa. Raguwar yawan noma, kaura daga karkara, da lalacewar ababen more rayuwa sun janyo koma baya a samar da kayayyaki da ƙaruwa a matakan talauci.

Masana sun jaddada cewa magance matsalar na buƙatar tsari mai faɗi.

Duk da cewa matakan soji na da muhimmanci, ana bukatar dogon lokaci na shirin farfaɗo da tattalin arziki, kyakkyawan shugabanci, tsaron al’umma ta hanyar haɗin gwiwa, da ingantaccen kula da iyakoki.

Ƙarfafa tattara bayanan sirri da kuma magance tushen talauci da wariya su ma na da muhimmanci wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

A ƙarshe, matsalar ’yan bindiga a Arewacin Najeriya ba batun tsaro kaɗai ba ne, illa babbar matsalar zamantakewa da tattalin arziki da ke buƙatar kulawa ta gaggawa da matakai masu dorewa.

Idan ba a ɗauki matakan da suka dace cikin haɗin gwiwa ba, lamarin na iya ƙara taɓarɓarewa tare da haifar da mummunan tasiri ga yankin da ƙasa baki ɗaya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here