Mahaifiyar Shahararriyar Mawakin Hausa da aka sace, Rarara ta shaki iskar ‘yanci

Rarara and his mother

Hajiya Hauwa’u Adamu, mahaifiyar fitaccen mawakin Hausa, Dauda Adamu, wanda aka fi sani da Rarara, ta shaki iskar‘yanci bayan shafe kwanaki 20 a hannunta masu garkuwa da mutane.

Rarara ne ya tabbatar da labarin sakin nata, a shafin sa na Instagram da aka tabbatar a safiyar Laraba.

Yayin da bayanai kan sakin mahaifiyar mai shekaru 75 ke ci gaba da yawo a kafafen sada zumunta, wasu rahotanni da ba a tabbatar ba sun ce an biya kudin fansa na wasu masu makudan miliyoyi kafin wadan da sukai garkuwar da ita su sake ta.

SolaceBase ta ruwaito cewa an sace Hajiya a jihar Katsina a watan da ya gabata.

A halin da ake ciki kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a baya ta sanar da kama wasu mutane biyu da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da ita.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here