Mahaifiyar Babban Editan Daily Trust ta rasu

IMG 20250623 WA0028

Hajiya Rabi Idris da ake kira da Hajiya Umma, mahaifiyar Babban Editan Daily Trust Malam Hamza Idris, ta rasu.

A cewar daya daga cikin ‘ya’yanta, Aminu Idris, ta rasu ne da safiyar yau Litinin, 23 ga watan Yuni, a gidanta da ke Kano sakamakon gajeriyar rashin lafiya.

Ya kara da cewa, za a yi jana’izar ta ne a makabartar Wali Maigeza wadda aka fi sani da Makabartar Kofar Mazugar a cikin birnin Kano.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here