karin kudin makaranta: ASUU ta bawa gwamanatin tarayya shawara

ASUU leader
ASUU leader

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya roki gwamnatin tarayya data sake duba karin kudin makaranta da tai a makarantun kasar nan.

Ya roki gwamnatin data yi hakan domin samin shugabanni masu inganci a nan gaba

Osodeke yana magana ne domin kalubalantar karin kudin makaranta da gwamnatin tarayya tayi a makarantun sakandare mallakinta, da kuma karin kudin makaranta da akai a manyan makarantun kasar nan.

Ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ranar Lahadi a Lagos cewa karin kudin makarantar barazana ne ga ya yan talakawa da suke karatu a kasar nan.

Idon za’a iya tunawa dai jami’ar lagos na daya daga cikin wadan da suka kara kudin makaranta a kasar nan, daga Naira N25,000 zuwa N200,000,  ya dan ganta da kos din da dalibi zai karanta.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here