Gwamnatin tarayya ƙarkashin jagorancin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta sake yin wani yunkuri na dakatar da yajin aikin da kungiyoyin kwadago ke shirin yi a fadin ƙasar nan, yayin da gwamnati ta gayyaci shugabannin kungiyar domin sake tattaunawa.
Za a gudanar da taron ne yau Lahadi, 1 ga watan Oktoba.
A wata takarda da wani darakta a ma’aikatar ƙwadago, Emmanuel Igbinosun, ya fitar a madadin ministan, ya mika wa shugaban kungiyar kwadago ta ƙasa (NLC), an gayyaci shugabannin kungiyar taro a fadar shugaban ƙasa a ranar Lahadi.
A ranar Juma’a 29 ga watan Satumba ne gwamnatin tarayya ta shirya wani taro da kungiyoyin kwadago, amma shugabannin kungiyar ba su halarta ba, kuma taron bai yiwu ba.













































