Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta mayar da taron majalisar zartarwa ta tarayya daga ranar Laraba zuwa Litinin.
Ministan yada labaran Najeriya Mohammed Idris ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron FEC da aka gudanar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Shugaba Tinubu dai ya gudanar da tarukan FEC sau biyu kacal tun bayan kaddamar da majalisar ministocinsa a watan Agusta.
Taron na FEC karo na biyu da aka gudanar a ranar litinin ya kuma sha rantsuwar rantsar da karin ministoci uku da majalisar dokokin kasar ta tantance a kwanakin baya.













































