Gwamnatin Filato ta saka dokar takaita zirga-zirga ta sa’a 24 a karamar hukumar Mangu

358644031 606129471691749 2721363008608619014 n
358644031 606129471691749 2721363008608619014 n

Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya sanya dokar takaita zirga-zirga ta sa’a 24 a karamar hukumar Mangu na jihar sakamakon hare-hare da suka janyo asarar rayuka da ma dukiyoyi a yankin.

Rikicin tsakanin wasu kabilu a yankin ya kuma raba mutane da dama yawa da muhallansu da kuma haifar da zaman dar-dar tskakanin kabilun fulani da kuma ta magafu.

Shugaban matasan Fulani ta Miyetti Allah a yankin na Mangu, Saidu Jauro ya fada wa BBC cewa al’ummar magafu sun kai hari a gidajen fulani tare da kona wasu, inda ya ce an kashe mutane 18 a garin Amsan.

Wani daga ɓangaren kabilar ta magafu da ake zargi da kai harin ya ce ‘a iya sanina ban san wani ɗan kabilar magafu da ya far wa fulani ba”.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here