Gwamna jihar Neja Umar Bago ya yi karatun baya wajen janye umarnin da ya bayar na cewa jami’an tsaro su kame duk wanda suka kama da askin Dada a kan sa musamman a birnin Minna babban birnin jihar.
Idan dai za a iya tunawa, Bago a lokacin da yake jawabi a taron tsaro na masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnati a ranar Talata, ya umurci jami’an tsaro da su yanke wa irin wadannan mutanen da aka kama hukunci tare da sanya musu tara.
“Duk wanda kuka same shi da tarin suma ta Dada ku kama shi, ya aske gashin”.
“Babu wanda ya isa ya yi kowane irin aski a cikin Minna, na ba jami’an tsaro umarnin daukar mataki,” in ji gwamnan.
Labari mai alaƙa: Gwamnatin jihar Neja ta bada umarnin kama mutanen da ke tara gashin Dada
Bayanin na farko, musamman wanda aka yi wa mutanen da ke fama da rawar kai, ya haifar da mummunar suka a shafukan sada zumunta da kuma sauran jama’a, wadanda suka zargi gwamnan da nuna wariya da rashin fahimtar dabarun yaki da laifuka.
Da yake mayar da martani kan lamarin ranar Laraba, Bago ya bayyana matsayarsa, inda ya ayyana filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu a matsayin madadin filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.
Ya ci gaba da bayyana mayar da martani a matsayin ” farfagandar kafofin watsa labaru “, ya kuma nanata cewa an yi kokarin aiwatar da aikin ne musamman ga kungiyoyin masu aikata laifuka.













































