Gwamanatin tarayya ta ayyana ranar Litinin, daya ga watan Mayu a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata.
Ministan harkokin cikin gida,Rauf Aregbesola, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da sakataran ma’aikar cikin gida, Shuaib Belgore ya sanyawa hannu a ranar Juma’a.
Ministan ya yabawa ma’aikata bisa sadakauwar da suke tare da aiki ba ji ba gani domin cigaban kasa Najeriya.
Ya kuma jin-jinawa jami’an tsaro bisa tarin nasarorin da suka samu wajan yaki da ta’addanci a fadin kasa baki daya.













































