FG Ta Dakatar Da Shirin N-Power, Ta Fara Gudanar Da Bincike

NPower
NPower

Gwamnatin tarayya ta ce ta dakatar da shirin N-Power har sai baba ta gani.

Ministar harkokin jin kai da yaki da fatara, Betta Edu, ta sanar da dakatarwar ne a ranar Asabar a wata hira da ta yi da gidan talabijin na TVC News.

A cewar Edu, an yanke hukuncin ne saboda wasu kura-kurai da aka samu a cikin shirin. A halin da ake ciki, ministan ta ce gwamnati ta fara gudanar da bincike kan yadda aka yi amfani da kudaden tun da aka fara shirin.

Ta bayyana cewa ba a samun wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin a wuraren da aka tura su aiki duk da haka suna tsammanin biyan alawus na wata-wata.

Ministan ta ce ya kamata wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin su fice daga shirin tun 2022 amma har yanzu suna kan biyan albashi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here