Mukaddashin Kwanturola Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Caroline Wura-Ola Adepoju, ta bayar da umarnin gudanar da bincike kan wasu korafe-korafe da ake yi wa jami’an hukumar a wasu ofisoshin fasfo na Najeriya.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar, DCI Aridegbe Adedotun ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.













































