Wani nau’in abib fashewa da ake zargin an dasa a wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, ya tashi a lokacin da masu ibada ke sallar Magariba da misalin karfe 6:00 na yamma.
Majiyoyi sun bayyana cewa masallacin yakan karɓi jama’a da dama, ciki har da ‘yan kasuwa da masu sayarwa da ke gudanar da harkokinsu a kasuwar Gamboru kullum.
Har zuwa lokacin da aka fitar da rahoton, babu wani bayani kai tsaye kan ko an samu asarar rayuka ko kuma rauni, kuma babu wata sanarwa ta hukuma kan lamarin.
Fashewar ta afku ne a wani birni da ya shafe kusan shekaru ashirin yana fuskantar tayar da kayar baya daga kungiyar Boko Haram da ISWAP lamarin da ya janyo mutuwar dubban mutane tare da tilasta wa miliyoyi barin muhallansu a yankin Arewa maso Gabas.
Babu wata kungiya da ta dauki alhakin harin, sai dai a baya mahara sun taba kai hari kan masallatai da wuraren da jama’a ke taruwa a Maiduguri ta hanyar kunar bakin wake da kuma na’urorin fashewa na gargajiya.
Kungiyar Boko Haram ta kaddamar da tayar da kayar baya a jihar Borno tun shekarar 2009 da nufin kafa daular Musulunci, kuma duk da hare-haren soji da hadin gwiwar kasashen yankin, hare-haren lokaci zuwa lokaci na ci gaba da barazana ga fararen hula a Arewa maso Gabas.
Reuters













































