Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB ta ce ba za ta sake tsawaita lokacin yin rajistar jarrabawar shiga manyan makarantu ta 2025 (UTME) ba bayan ranar 8 ga watan Maris.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Dr Fabian Benjamin ya rabawa manema labarai a Abuja ranar Talata.
Benjamin ya ce wa’adin rajistar da ya fara a ranar 3 ga Fabrairu, zai kare ne a ranar 8 ga Maris, 2025.
A cewarsa, an sanar da wannan wa’adin a fili a duk tallace-tallace da kalandar hukuma don fara aikin UTME na 2025.
Ya kara da cewa a halin yanzu, sama da dalibai miliyan 1.5 ne suka yi nasarar yin rajista, wadanda suka yi daidai da hasashen hukumar a 2025.
Benjamin ya karfafa wa dalibai gwiwa da su kammala rajista da wuri tare da bin ka’idojin da aka kayyade na jarrabawar UTME 2025. (NAN)













































