Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta ce za a fara aiwatar da tsarin koyar da karatu mafi kankanta na (CCMAS) nan da Satumbar 2023.
Ana sa ran CCMAS za ta jagoranci wajen tsara manhajoji don shirye-shiryensu tare da kawo sabbin abubuwan da suka dace domin bunkasa ilimi a fadin kasa baki daya.
Da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan CCMAS a Abuja ranar Laraba, Mukaddashin Sakataren Hukumar NUC, Chris Maiyaki ya ce tsarin zai mayar da jami’o’in Najeri suyi fice a Afirka.
A cewarsa, aiwatar da aikin zai taimaka wajen kara kaimi ga fannin ilimi a nan gaba.












































