Gwamnatin Nasarawa ta dakatar da MD kan zargin lalata allunan kamfe

cb00962dc9736047
cb00962dc9736047

Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya amince da dakatar da Alhaji Mohammed Wada-Yahaya, Manajan Daraktan Hukumar Raya Birane ta Jihar Nasarawa bisa zargin lalata allunan yakin neman zabe.

Dakatarwar na kunshe ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun Sakataren Gwamnatin jihar Malam Muhammed Ubandoma a Lafia.

Sanarwar ta kara da cewa MD na kan dakatarwa ba tare da biyan albashi ba har sai an kammala bincike kan lamarin.

“Akwai jerin korafe-korafe game da lalata allunan talla da ‘yan siyasa da magoya bayansu suka kafa ba gaira ba dalili; da nufin yin katsalandan a zaben 2023, ciki har da jam’iyya mai mulki.

“Lalata allunan talla ba tare da wani dalili ba, daidai yake da rashin biyayya da rashin da’a,” in ji gwamnati.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here