Shugaban Kwamitin Hadin Gwiwa dake Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi, Muhuyi Magaji Rimin Gado Esq, ya kaddamar da kananan kwamitoci tara wadanda aka dorawa alhakin karfafa yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Jihar Kano.
A cikin sanarwa da Lamara Garba, mamban kwamitin yada labarai da hulda da jama’a na kwamitin ya fitar ranar Asabar, ta ce an gudanar da rantsuwar ne a ranar Juma’a, inda Shugaban ya bukaci mambobin kwamitocin da su nuna kwazo, sadaukarwa da azama wajen gudanar da ayyukansu.
Muhuyi ya tunatar da mambobin kwamitocin girman aikin da ke gabansu, inda ya jaddada cewa nasarar hukumar gaba daya ta dogara ne kan muhimmanci da kwazon da kowane kwamiti zai bayar ga aikinsa.
Ya bukaci mambobin da su ninka kokarin su, su yi aiki tare a matsayin kungiya, kuma su tsaya tsayin daka kan manufofin hukumar, tare da bayyana cewa yaki da sha da fataucin kwayoyi yana bukatar jajircewa mai dorewa, kyakkyawan tsari da kuma raba aiki a tsakani.
A cewarsa, an kafa kwamitocin ne domin samar da tsari mai kyau kuma na musamman don tunkarar bangarori daban-daban na matsalar kwayoyi, tare da tabbatar da cewa dukkan masu ruwa da tsaki sun yi aiki tare domin samun sakamako mai dorewa.
SolaceBase ta ruwaito cewa kwamitoci tara da aka kaddamar sun hada da Kudi, Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Wayar da Kai, Lasisi, Kaya da Tabbatarwa, Bin Dokoki, Bincike da Sanya Ido, Jagoranci da Aiwatarwa, Leken Asiri, Gyaran Hali da Majalisar Sarakunan Gargajiya da kuma Kwamitin Daidaita Yaki da Miyagun Kwayoyi.
Tsarin ya kuma samar da ayyukan da aka tsara da kyau a dukkan fannoni daban-daban na daukar matakai.
Shugaban ya bukaci mambobin da su dauki nadin na su a matsayin wata hidima ga kasa maimakon matsayin aiki kawai, inda ya jaddada cewa nauyin da aka dora musu yana bukatar horo, kwarewa da kuma sadaukarwa ga muradun bai-daya.












































